A Nigeria Mutane 239 Yan Bindiga suka kashe a wata guda – Bincike

Date:

A cikin mako guda, an kasha mutane akalla 239 a Najeriya da suka hada da jami’an tsaro, sannan aka yi garkuwa da 44, lamarin da ke dada fito da matsalar tsaron da kasar ke fama da ita.

An yi kisan ne a sassan kasar da suka hada da babban birnin tarayya Abuja da ke zama fadar gwamnatin Nigeria.

Alkaluman da aka tattara sun nuna cewa, an kashe mutane 20 a ranar Lahadi ta makon Daya gabata, 5 a ranar Litinin, sai 6 a ranar Talata, inda aka kashe 85 a ranar Laraba a Karamar Hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Shafin Radio Farance ya rawaito cewa an salwantar da rayukan mutane 60 a kauyen Magami a ranar Juma’ar da ta gabata.

Haka ma wasu dalibai 3 na Jami’ar Greenfiled mai zaman kanta a jihar Kaduna sun rasa rayukansu bayan ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su, yayin da wasu jami’an ‘yan sanda a jihar Anambra su ma suka mutu a wani farmaki da aka kaddamar kan shalkwatansu.

Hare-hare a sassan Najeriya sun tsananta, inda ‘yan bindiga ke far wa kauyuka da kasuwanni da wuraren ibada har ma da matafiya da ke bin babbar hanya.

77 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...