Mutanen gari sun kama ’yan bindiga a Zariya

Date:


Mutanen gari sun yi kukan kura sun cafke masu garkuwa da mutane da suka kai hari a unguwar Low Cost da ke Zariya.

A halin yanzu, wasu daga cikin ’yan bindigar suna hannun ’yan sanda bayan da mutanen unguwar suka yi musu kofar rago ranar Lahadi da tsakar dare.


Duk da haka, masu garkuwar sun tafi da matan aure biyu daga gidaje daban-daban, amma sun sako kananan yara biyun da suka dauka da tare da daya daga cikin matan, sai dai ba su sako mahaifiyar yaran ba.

Majiyarmu a Zariya ta ce ’yan bindigar sun harbi kananan yara almajirai guda hudu a lokacin farmakin da suka kai.

Daily Trust ta gana da almajiran da raunukan harin a jikinsu, kuma a halin yanzu suna samun kulawa a asibitin New City da ke a Zariyan.

74 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...