A Nigeria Mutane 239 Yan Bindiga suka kashe a wata guda – Bincike

Date:

A cikin mako guda, an kasha mutane akalla 239 a Najeriya da suka hada da jami’an tsaro, sannan aka yi garkuwa da 44, lamarin da ke dada fito da matsalar tsaron da kasar ke fama da ita.

An yi kisan ne a sassan kasar da suka hada da babban birnin tarayya Abuja da ke zama fadar gwamnatin Nigeria.

Alkaluman da aka tattara sun nuna cewa, an kashe mutane 20 a ranar Lahadi ta makon Daya gabata, 5 a ranar Litinin, sai 6 a ranar Talata, inda aka kashe 85 a ranar Laraba a Karamar Hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Shafin Radio Farance ya rawaito cewa an salwantar da rayukan mutane 60 a kauyen Magami a ranar Juma’ar da ta gabata.

Haka ma wasu dalibai 3 na Jami’ar Greenfiled mai zaman kanta a jihar Kaduna sun rasa rayukansu bayan ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su, yayin da wasu jami’an ‘yan sanda a jihar Anambra su ma suka mutu a wani farmaki da aka kaddamar kan shalkwatansu.

Hare-hare a sassan Najeriya sun tsananta, inda ‘yan bindiga ke far wa kauyuka da kasuwanni da wuraren ibada har ma da matafiya da ke bin babbar hanya.

77 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...