Tsohon Sarkin Kano Muhd Sanusi II ya Mika ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyar Sarakunan Kano da Bichi

Date:

Tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya aike d sakon ta’aziyyarsa na mutuwar Hajiya Maryam Ado Bayero ga al’ummar jihar Kano baki daya.

A wani bidiyo da yake yawo a dandalin sada zumunta na zamani, wanda aka saka shi a shafinsa Mai Suna Muhammadu Sanusi II Wanda ya yi magana game da babban rashin da aka yi a Kano.

Da yake jawabi a Bidiyon, Malam Sanusi II ya ce: “Yau mun tashi da rasuwar mahaifiyarmu, Maryam Bade (Ado Bayero), uwargidar marigayi Sarki Ado Bayero.”

Mai martaban ya cigaba da cewa: “Ta rasu a kasar Masar, mu na mika ta’aziyya ga daukacin al’umma.”

A wannan bidiyo da aka wallafa a shafin Muhammadu Sanusi II ya yi wa marigayiyar addu’a tare da sauran jama’a.

“Allah ya sa ta huta, Allah ya sa ciwon da ta yi ya zama kaffara.” Sanusi ya ke cewa za ayi rashin mahaifiyar magajinsa da kuma Sarki Nasiru Ado Bayero.

Malam Sanusi II wanda ya bar karagar mulki a bara ya sa an yi wa marigayiyar salatin Annabi SAW kafa 10 da karatun suratul Ikhlas domin ta samu ceto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...