Hukumar Kashe Gobara ta jihar Kano ta Koka

Date:

Daga Nura Bala Ajingi

Hukumar kashe Gobara da kai agajin gaggawa ta jahar kano ta danganta asarar rayuka da dukiya akan rashin tanadar lambobinta na kiran neman dauki har sai idan iftila’i ya faru.

Babban Daraktan hukumar Alh. Hassan Ahmed Mohd ya bayyana haka a ganawarsa da manema labarai a ofishinsà.

Ya ce kame kamen neman lambar hukumar a lokacin da iftila’i ya faru yana kawo jinkiri wajen kai dauki wadda hakan ke haifar da asarar rayuka da dukiya.

Shugaban ya yi kira ga al’umma da su rika ajiye lambobin hukumar kafin bukatarsu ta zo domin ceton rayukan al’umma da dukiya akan lokaci.

Lambobin da za a nemi hukumar su ne 08098822631 da 07026026400 da kuma 07051246833

Shugaban hukumar kashe gobarar ta jahar kano ya kuma bukaci masu ababan hawa akan titi da su rika baiwa jami’an hukumar hanya a duk lokacin da suka fita kai agajin gaggawa.

Alh. Hassan Ahmed Mohd ya yabawa gwamnatin jahar kano bisa jagorancin gwamna Abdullahi Umar Gandue saboda gagarumar gudummawar da take baiwa hukumar wajen gudanar da aiyukanta.

Daga bisani ya kuma nuna gamsuwarsa bisa yanda jami’an tsaro da al’umar jahar kano suke ba su hadin kai sannan ya godewa wadanda suka yi musu ta’aziyyar jami’ansu biyu da suka rasu tare da jajanta musu dangane da gobarar da ta shafi jami’ansu a gidan mai na Al’ihsan a unguwar sharada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...