Tsadar Abinci: Muhuyi Magaji ya gana da Masu shinkafa a Kano

Date:

A yau ne Shugaban hukumar Karbar korafe-korafe da hana ayyukan cin hanci da rashawa ta jahar Kano, Barrister Muhuyi Magaji Rimin Gado ya gana da Shugabancin kungiyar masu kamfanonin Sarrafa shinkafa ta kasa reshen jahar Kano, kan yadda za a magance matsalar tsadar shinkafar a jahar Kano.

A yayin zaman Barrister Muhuyi Magaji ya jagoran ta, Shugabancin kungiyar sun koka kan tashin gwauron zabi da dukkanin bangarorin kayan ayyukan su suka yi tare da neman hukumar ta shiga tsakani don samun rangwame daga gwamnatin tarayya.

A karshe Barrister Muhuyi ya basu tabbacin yin iya bakin kokarinsa domin ganin an saukaka wa Jama’a wahalar tsadar kayan abinci musamman ma shinkafa.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito yadda Kayan Abinchi sukai tashin gwauron zabi Musamman a yan kwanakinan.

63 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...