Yan Kabilar Igbo Sun Baiwa Shugaban Ma’aikatan Kano Usman Bala Sarauta

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Sarkin kabilar Igbo a nan Kano Boniface Ibekwe Ezedioranma, ya nada Shugaban Ma’aikatan jihar Kano Kuma shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnati Alhaji Usman Bala Muhammad a matsayin jakadan zaman lafiya na kabilar Ibo mazauna Kano.

 

Nadin ya gudana da yammacin yau lahadi a filin wasa na Ado Bayero square dake unguwar sabon gari a yankin Karamar hukumar Fagge.

Talla

Dayake jawabi Bayan nadin shugaban Ma’aikatan Jihar Kano Alhaji Usman Bala Muhammad,ya bayyana cewar zaman lafiya da kulawar da Gwamnatin Kano ke bawa Sauran kabilu na daga cikin dalilan da Sarkin kabilar ta Ibo ya duba tare da bashi wannan sarauta.

2023: Siyasar Kano na kokarin shiga mawuyacin hali

Usman Bala Muhammad,ya Kuma Kara da cewar wannan sarauta zata Kara kawo hadin kai da zaman lafiya tsakanin sauran kabilu dake fadin kasar nan.

 

Usman Bala lokacin da ake nada shi a sarauta

Yayin taron an kuma karrama Alhaji Abubakar Isah da kuma dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Fagge Aminu Sulaiman Goro da sarauta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...