Yan Kabilar Igbo Sun Baiwa Shugaban Ma’aikatan Kano Usman Bala Sarauta

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Sarkin kabilar Igbo a nan Kano Boniface Ibekwe Ezedioranma, ya nada Shugaban Ma’aikatan jihar Kano Kuma shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnati Alhaji Usman Bala Muhammad a matsayin jakadan zaman lafiya na kabilar Ibo mazauna Kano.

 

Nadin ya gudana da yammacin yau lahadi a filin wasa na Ado Bayero square dake unguwar sabon gari a yankin Karamar hukumar Fagge.

Talla

Dayake jawabi Bayan nadin shugaban Ma’aikatan Jihar Kano Alhaji Usman Bala Muhammad,ya bayyana cewar zaman lafiya da kulawar da Gwamnatin Kano ke bawa Sauran kabilu na daga cikin dalilan da Sarkin kabilar ta Ibo ya duba tare da bashi wannan sarauta.

2023: Siyasar Kano na kokarin shiga mawuyacin hali

Usman Bala Muhammad,ya Kuma Kara da cewar wannan sarauta zata Kara kawo hadin kai da zaman lafiya tsakanin sauran kabilu dake fadin kasar nan.

 

Usman Bala lokacin da ake nada shi a sarauta

Yayin taron an kuma karrama Alhaji Abubakar Isah da kuma dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Fagge Aminu Sulaiman Goro da sarauta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...