Yan Kabilar Igbo Sun Baiwa Shugaban Ma’aikatan Kano Usman Bala Sarauta

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Sarkin kabilar Igbo a nan Kano Boniface Ibekwe Ezedioranma, ya nada Shugaban Ma’aikatan jihar Kano Kuma shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnati Alhaji Usman Bala Muhammad a matsayin jakadan zaman lafiya na kabilar Ibo mazauna Kano.

 

Nadin ya gudana da yammacin yau lahadi a filin wasa na Ado Bayero square dake unguwar sabon gari a yankin Karamar hukumar Fagge.

Talla

Dayake jawabi Bayan nadin shugaban Ma’aikatan Jihar Kano Alhaji Usman Bala Muhammad,ya bayyana cewar zaman lafiya da kulawar da Gwamnatin Kano ke bawa Sauran kabilu na daga cikin dalilan da Sarkin kabilar ta Ibo ya duba tare da bashi wannan sarauta.

2023: Siyasar Kano na kokarin shiga mawuyacin hali

Usman Bala Muhammad,ya Kuma Kara da cewar wannan sarauta zata Kara kawo hadin kai da zaman lafiya tsakanin sauran kabilu dake fadin kasar nan.

 

Usman Bala lokacin da ake nada shi a sarauta

Yayin taron an kuma karrama Alhaji Abubakar Isah da kuma dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Fagge Aminu Sulaiman Goro da sarauta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...