Bichi da makwabtan ta zasu yi adabo da matsalar wutar lantarki – Engr. Abba Bichi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

 

A jiya alhamis ne zababben dan majalisar Tarayya Mai Wakiltar Bichi, kuma shugaban kwamitin ayyuka na majalisar tarayya Engr. Abubakar Kabir Abubakar ya jagoranci ma’aikatan Hukumar TCN da KEDCO domin kunna wutar Lantarki a sabon gidan wuta daya kawo Kuma yadaukin nauyin duk aikace-aikacen da akayi da kuma Katangeshi a karamar hukumar Bichi.

 

“Gidan wutar zai dauki kananan Hukumomi 14 dake kewaye da Bichi awa 24 idan ta dauke toh sede matsala ce daga National grid”. Inji Abba bichi

 

Yayin da yake jawabi a wajen taron kunna wutar Engr. Abubukar Bichi yace an samar da aikin wutar lantarkin ne domin inganta rayuwar al’ummar bichi da kewaye da kuma kara bunkasa tattalin arzikin yankin.

 

Talla

Ya ce idan wutar lantarki ta fara aiki gadan-gadan al’ummar yankin zasu yi adabo da matsalolin hasken wutar lantarki, kuma zai samar da aiyukan yi ga matasa masu yawa sosai.

 

Hukumar TCN ta yabawa Dan Majalisar bisa yadda ya fitar dasu kunya ya dauki nauyin aikin da za’ayi shekaru dayawa anayi amma yayi musu a Kasa da shekara 2 a don haka suka ce a sanyawa gidan wuta suna Abubakar Kabir Abubakar Sub-Station Bichi.

Sabuwar tashar wutar lantarki dake Bichi

Za dai ayi babban bikin bude wannan gidan wuta a wata ne watan December, inda ake sa ran Ministan Wutar lantarki da MD na TCN da Gwamnan Jihar Kano da Mai Martaba Sarkin Bichi zasu Jagoranci budewa katafaren tashar wutar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...