Wata mata ta haihu a masallacin Annabi a Madina

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Jami’an ƙungiyar agaji ta Red Crescent sun karɓi haihuwar wata mata da naƙuda ta tasar mata a Masallacin Manzon Allah (S A W) da ke Madina.

 

Shafin da ke kula da masallatai biyu masu daraja na Saudiyya Haramain Sharifain ne ya wallafa labarin a shafinsa na Facebook a yau Juma’a.

Talla

Jami’an Red Crescent din sun je ne bayan kiran gaggawa da aka yi musu.

Bamu janye tuhumar da muke yiwa Tukur Manu ba – DSS

Bayan nan ne kuma sai aka kai mai jegon da jaririnta wani asibiti Jibril Health Center don ci gaba da kula da su.

 

Mahaifin jaririyar tuni ya raɗa mata suna Taiba, kamar yadda shafin ya ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...