Wata mata ta haihu a masallacin Annabi a Madina

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Jami’an Ζ™ungiyar agaji ta Red Crescent sun karΙ“i haihuwar wata mata da naΖ™uda ta tasar mata a Masallacin Manzon Allah (S A W) da ke Madina.

 

Shafin da ke kula da masallatai biyu masu daraja na Saudiyya Haramain Sharifain ne ya wallafa labarin a shafinsa na Facebook a yau Juma’a.

Talla

Jami’an Red Crescent din sun je ne bayan kiran gaggawa da aka yi musu.

Bamu janye tuhumar da muke yiwa Tukur Manu ba – DSS

Bayan nan ne kuma sai aka kai mai jegon da jaririnta wani asibiti Jibril Health Center don ci gaba da kula da su.

 

Mahaifin jaririyar tuni ya raΙ—a mata suna Taiba, kamar yadda shafin ya ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related