Da dumi-dumi: Buhari ya amince da karin albashi ga alkalai

Date:

Daga Aliyu Nasir Zangon Aya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da kuma bada umarnin a dauki matakan gaggawa wajen aiwatar da shirin inganta albashi da jin dadin ma’aikatan shari’a.
 Shugaban  Buhari ya bayyana haka ne a ranar Juma’a, a wajen bikin kaddamar da Nabo Graham-Douglass Campus na makarantar koyon aikin shari’a ta Najeriya da ke Fatakwal ga majalisar ilimin shari’a.
Talla
 Babban Lauyan kasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN ne ya wakilci Shugaban kasa Muhammadu Buhari a wajen taron.
 Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Dr. Umar J|ibrilu Gwandu, mataimakin na musamman kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, a ofishin babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a.
 A cewar sanarwar, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umurci shugaban hukumar tattara kudaden shiga da ta rabon arzikin kasa da babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a da su gaggauta fara daukar matakan tabbatar da aiwatar da shirin inganta albashi da walwala ga jami’an shari’a. kasa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...