Da dumi-dumi: Buhari ya amince da karin albashi ga alkalai

Date:

Daga Aliyu Nasir Zangon Aya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da kuma bada umarnin a dauki matakan gaggawa wajen aiwatar da shirin inganta albashi da jin dadin ma’aikatan shari’a.
 Shugaban  Buhari ya bayyana haka ne a ranar Juma’a, a wajen bikin kaddamar da Nabo Graham-Douglass Campus na makarantar koyon aikin shari’a ta Najeriya da ke Fatakwal ga majalisar ilimin shari’a.
Talla
 Babban Lauyan kasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN ne ya wakilci Shugaban kasa Muhammadu Buhari a wajen taron.
 Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Dr. Umar J|ibrilu Gwandu, mataimakin na musamman kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, a ofishin babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a.
 A cewar sanarwar, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umurci shugaban hukumar tattara kudaden shiga da ta rabon arzikin kasa da babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a da su gaggauta fara daukar matakan tabbatar da aiwatar da shirin inganta albashi da walwala ga jami’an shari’a. kasa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...