2023: Alaramma Ahmad Sulaiman ya magantu kan batun yiwa yan takarar addu’a akan duro

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shahararren malamin addinin musuluncin nan wanda ya shahara wajen karanta al-qur’ani Mai girma a kano da kasa baki daya, Alaramma Ahmad Sulaiman ya ce masu ganin laifinsa don ya yiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Tinubu addu’a a wajen yakin neman zaben da aka yi a Jos kawai mahassada ne da kuma wadanda basu fahimci yadda rayuwa take ba.

 

“ Shigar da muke yi harkokin siyasa ta taimaka wajen cigaban addinin Musulunci a arewacin Nijeriya dama kuma mun shiga siyasar ne don kare kimar addinin Musulunci” inji Alaramma Ahmad Suleiman

Talla

 

Alaramma Ahmad Sulaiman ya bayyana hakan ne cikin wata hira ta musamman da sukai da shafin DCL Hausa a ranar Juma’ar nan.

 

” Banga abun da yasa mutane suke damuwa ba saboda da na yiwa Tinubu addu’a, idan aka lura a baya na yiwa Kwankwaso na yiwa Ganduje da Sule lamido, sannan kuma na yiwa Atiku Abubakar, Amma duk ba wanda ake zance akan sa sai na Tinubu na rasa me yasa”. A cewar Ahmad Sulaiman

 

 

Yace al’umma da dama basu fahimci dalilin su na shiga Siyasa ba, Inda shi dai ya shiga siyasa ne don ya kare Martabar addinin musulunci kuma kundin tsarin mulkin kasa ya baiwa Malaman addinin musulunci damar shiga siyasa kamar kowa .

Malam Ahmad Sulaiman a Jos yayin taron Bola Tinubu

” Allah yace Malamai su ne managarta a Cikin al’umma to so kuke mutanen kirki su ki shiga Siyasa Saboda mutanen daba na kwarai ba su shiga don su sami dama su cutar da al’umma, ba yau na fara Siyasa ba kuma bazan daina ba”. Inji malamin

 

Daga ƙarshe yace ya rasa dalilin da yasa mutane suka damu dan ya yiwa Bola Tinubu addu’a, shi na gamsu zai taimaki Musulunci shi yasa nake binsa yakin neman zabe Kuma ma Ina da mukami da kwamitin yakin neman zaben sa”.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...