2023: An kara tsaurara matakan tsaro a ofisoshin INEC dake Nigeria

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Gwamnatin Najeriya ta tura jami’an tsaro na DSS da sojoji da jami’an hukumar kashe gobara ofisoshin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC domin tsaurara tsaro gabannin zaɓen 2023.

Ta kuma umarci jami’an su inganta tattara bayanan sirri domin daƙile duk wani yunƙuri na rikici ko ɓata gari a makonni masu zuwa gaba.
Talla
Babban Sufeta Janar na ‘yan sanda kasar, Usman Baba ne ya shaida hakan bayan tattaunawa da shugabanni jam’iyyun siyasa a hedikwatar ‘yan sanda da ke Abuja.
Rundunar ta ce a cikin mako shida, an samu rigingimu aƙalla 52 a sassa daban-daban na ƙasar da suka haɗa da Ogun da Osun.
Akwai kuma harin da aka kai wa magoya-baya a gangamin yaƙin neman zaɓe a jihohi irinsu Borno da Kaduna da Zamfara da dai sauransu.
Rundunar ta ce tana tsare da wasu da ake zargi na da hannu a waɗannan rikice-rikice, kuma za a gurfanar da su domin fuskantar hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...