2023: An kara tsaurara matakan tsaro a ofisoshin INEC dake Nigeria

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Gwamnatin Najeriya ta tura jami’an tsaro na DSS da sojoji da jami’an hukumar kashe gobara ofisoshin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC domin tsaurara tsaro gabannin zaɓen 2023.

Ta kuma umarci jami’an su inganta tattara bayanan sirri domin daƙile duk wani yunƙuri na rikici ko ɓata gari a makonni masu zuwa gaba.
Talla
Babban Sufeta Janar na ‘yan sanda kasar, Usman Baba ne ya shaida hakan bayan tattaunawa da shugabanni jam’iyyun siyasa a hedikwatar ‘yan sanda da ke Abuja.
Rundunar ta ce a cikin mako shida, an samu rigingimu aƙalla 52 a sassa daban-daban na ƙasar da suka haɗa da Ogun da Osun.
Akwai kuma harin da aka kai wa magoya-baya a gangamin yaƙin neman zaɓe a jihohi irinsu Borno da Kaduna da Zamfara da dai sauransu.
Rundunar ta ce tana tsare da wasu da ake zargi na da hannu a waɗannan rikice-rikice, kuma za a gurfanar da su domin fuskantar hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...