Ganduje ya mika ta’aziyyarsa bisa rasuwar tsohon dan bal din Kano Pillars Bello K/mata

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamnan jihar kano Abdullahi Umar Ganduje ya mika ta’aziyyarsa bisa rasuwar tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars Bello Musa Kofar Mata, wanda ya rasu kwanan nan. Wanda ya rasu yana da shekaru 34 a duniya.

 

Gwamna Ganduje ya mika sakon ta’aziyyar ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaransa Malam Abba Anwar ya fitar kuma ya aikowa kadaura24.

Talla

 

Yayin da yake addu’ar Allah ya jikan dan wasan wanda ya fara wasan kwallon kafa a Buffalo FC Kano, Kano Pillars FC, Heartland FC of Owerri, FC Ifeanyi Uba na Nnewi da Elkanemi Warriors na Maiduguri, ya mika sakon ta’aziyya ga kungiyar da kuma dangin marigayin.

 

Ya ce ya kadu Sosai da samu labarin rasuwar,Inda yayi fatan Allah ya jikansa da rahama, yace rashin Bellon babban rashi ne ga daukacin Masu harkokin kwallon kafa a Kano da kasa baki daya.

 

Ganduje ya kara da cewa, a madadin gwamnati da na al’ummar jihar Kano, yana mika sakon ta’aziyyarsa da addu’o’i na musamman ga Allah madaukakin sarki ya gafarta masa yasa aljanna ta zamo makomarsa.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...