Za a rage sadaki da kudin biki a China

Date:

Daga Khadija Abdullahi

 

Gwamnatin China ta kaddamar da wani gangami na rage yawan kudin da ake kashewa a yayin biki da kuma rage sadaki.

Gwamnatin ta yi hakan ne a wani bangare na yunkurin dakatar da raguwar da ake samu a yawan masu aure abin da kuma ya janyo raguwar haihuwa.

Talla

Kungiyoyi da dama ne suka shiga gangamin, da nufin janyo hankalin mutane a kan rage almubazzaranci yayin biki.

 

Gwamnatin ta ce idan an rage yawan kudin da ake kashewa a lokacin biki za a samu karuwar masu yin aure a kasar.

Talla

 

To sai dai kuma masu sharhi sun ce da wuya wannan yunkuri ya yi tasiri, saboda raguwar da al’ummar kasar ke yi ya sa mutane kalilan ne zasu kai shekarun aure.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...