Daga Auwal Alhassan Kademi
Wata kungiya mai suna “Mu taimaki juna” dake garin Gwagwarwa a karamar hukumar Nasarawa Kano ta gudanar da aikin feshin magani Sauro a unguwar a wani matakin na takaita yaduwar cutar zazzabi cizon Sauro a Kano.
Jim kadan bayan kammala aikin feshin a zantawarsa da wakilin Kadaura24, Shugaban kungiyar Com. Abubakar Idris Gwagwarwa, yace sun gudanar da aikin ne domin magance matsalar zazzabin cizon saura da ya addabi al’umma a wannan lokaci.
Yace dama duk shekara sukan gudanar da aikin, Inda suke shiga lungu da sako na yankin tare da shiga Gida-gida don yin feshi a bandakuna domin kashe duk wasu sauraye dake cutar da al’umma.

” Mun kirkiri wannan kungiya ne ta “mu taimaki juna” saboda mu rika gudanar da irin wadannan aiyuka don inganta Muhallanmu da Kuma taimakawa junanmu, saboda idan muka ce komai sai gwamnati ta yi mana to Zamu dade cikin matsaloli”. Inji Abubakar Idris
Shugaban kungiyar ya kuma kara da cewa su kan sayi magani cutar zazzabin cizon saura don rabawa ga marasa karfi dake yankin, sannan yace su kan share Kuma su kwashe shara a magudanan ruwa.

” Yadda mukai wannan aikin a Wani yanki na Gwagwarwa Muna sa ran nan gaba zamu Kara fadada aikin zuwa dukkanin unguwannin dake karkashin garin dagaci Gwagwarwa, don bada misali ga saura. Matasa don suma su yi koyi”.
Yace karo-karo su ke yi don tara kudaden da suke sayo kayan da suke aikin da su, don haka ya bukaci Masu rike da mukaman gwamnati da masu hannu da shuni da su rika tallafawa kungiyoyi irin nasu don ciyar da al’umma gaba.