Sallah: Shugaban K/H Rano ya gargadi matasan yankin kan zaman lafiya

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Shugaban karamar hukumar Rano Malam Naziru Yau, ya yi kira ga al’ummar yankin da su tabbatar sun gudanar da bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali da lumana,

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito makonni biyu da suka gabata an sami tashin hankali a garin Rano wanda ya yi sanadiyyar mutuwar DPO na garin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Shugaban karamar hukumar wanda yayi magana ta bakin kakakin karamar hukumar Rano Rt. Hon. Ahmed Abdullahi Jibrin, ya bukaci al’ummar Rano da su manta da abun da ya faru, su rungumi zaman lafiya, hadin kai,da tsoron Allah musamman a Wannan lokaci na Sallah.

Sallah: Kar ku bari a yi amfani da ku wajen tashin hankalin al’umma -Sakon Kungiyar ONE KANO AGENDA ga matasa

“Ina kira ga matasanmu, malaman addini, sarakunan gargajiya, da masu ruwa da tsaki da su tabbatar da cewa ba a sami tashin hankali ba a bikin sallar dake tafe ba.”

Shugaban ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa an samar da isassun matakan tsaro don kare rayuka da dukiyoyin al’umma alokacin bukukuwan. Ya kuma yi kira ga daukacin al’umma da su ba jami’an tsaro cikakken hadin kai.

InShot 20250309 102403344

A wata sanarwa da jami’in yada labarai na shiyyar Rano Rabi’u Khalil Kura ya aikowa Kadaura24, ya ce Shugaban ua yabawa gwamna Abba Kabeer Yusuf bisa yadda yake samar da ababen more rayuwa da Jagoranci na gari da yake yi a jihar Kano.

Ya kuma bai wa al’ummar yankin tabbacin gwamnatin sa za ta cigaba da samar da karin kayan more rayuwa, ya kuma bukace su da su ci gaba da yi wa kasa addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...