Kansila a K/H Garum Mallam ya rabawa marayu 300 kayan Sallah

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Sama da yara mayaru 300 ne su ka karbi tallafin suturu na maza da mata a karamar hukumar Garun mallam.

Da ya ke mika tallafin kansilan Noma na karamar hukumar Alh Abdurrashid Umar Dan’asabe Garun mallam ya ce sun rabawa marayun kayan ne duba da irin halin da wasu ke shiga na damuwa musamman a lokuntan bikin sallah ya sa ya ke bada gudunmawarsa ga marayu don rage masu damuwa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

” Wannan lokaci ne na farin ciki da ya kamata su ma yara marayu su kasance cikin farin ciki, kamar yadda yara masu iyaye suke kasancewa”. Dan asabe

Sallah: Kar ku bari a yi amfani da ku wajen tashin hankalin al’umma -Sakon Kungiyar ONE KANO AGENDA ga matasa

Kansilan Noman, daga ya kuma bukaci sauran al’umma da su rinka daurewa daga dan abun da Allah ya huwace musu domin taimakawa marayun yankunansu.

Mariya Sani, na daya daga cikin wadan da suka karbi tallafin atamfa kuma ta godewa Kansilan Noma Abdurrashid bisa sa su cikin masu farin ciki a babbar sallah.

InShot 20250309 102403344

Daga cikin wadan da su ka halaci bikin bada tallafin akwai masu girma mataimakin shugaban karamar hukumar Alh Tasiu Sale Kwiwa da kansilolin karamar hukumar da malamai da sauran al’umma gari baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...