Daga Zainab Muhd Darmanawa
Kwamishiniyar kula da harkokin mata ta jihar Kano Dr Zahra’u Muhammad ta ce tuni shirye-shirye suka yi nisa na sake Gudanar da auren zawarawa da ‘yan mata a jihar.
Cikin Sanarwar da Jami’ar yada labaran Ma’aikatar Bahijja Malam Kabara ta aikowa Kadaura24 ta ce Malam Zahra’u ta bayyana hakan ne a yayin wani taron daurin aure na mutane 31 maza da mata, wanda aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha.
Kwamishiniyar ta sake jaddada kudirin gwamnatin kano na shirya irin wannan aure, inda ta bayyana kalubalen tattalin arziki tun daga lokacin COVID-19 a matsayin daya daga cikin manyan kalubalen da suka jinkirta shirin.
Dr Zahra’u Muhd ta kuma bayyana cewa Insha Allahu shirin zai gudana ne ta hanyar ma’aikatar kula da mata, kuma zata zabi marayu da marasa galihu.
Daga nan sai ta bukaci ma’aurata da su yi biyayya ga juna, kuma su bi ka’idojin aure Kamar yadda yake a Musulunci.
Daga nan ta yaba da kokarin Gidauniyar FOMWAN DA DARUL ARQAM da suka shirya taron tare da yin kira ga sauran kungiyoyi masu zaman kansu da su yi koyi da wannan kyakkyawan misali.