Furodusa Abubakar mai shadda na shirin angwancewa da Jaruma Aisha Humaira

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

Kyawawan hotunan kafin aure Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jaruma Aisha Ahmad Idris wacce aka fi sani da Aishatul Humaira sun karade shafukan Sada Zumunta na Facebook da Instagram a safiyar alhamis din nan.

Kadaura24 ta rawaito tun farko dai, an fara rade-radin cewa Furodusan zai angwance a watan Maris, sai dai kuma ba a bayyana wacece amaryar ba.
Da kanshi ya je shafinsa na Instagram inda ya sanar da cewa zai yi wuff da jakadiyar gishirin Dangote tare da saka hotunansu na kafin aure.
A safiyar Alhamis ne aka wayi gari da sabbin kyawawan hotunan kafin aure na furodusa a masana’antar Kannywood, Abba Bashir Maishadda da jaruma Aishatul Humaira.
Tun farko dai, shafin Labaran Kannywood a Twitter a kwanaki biyu da suka gabata sun bayyana cewa furodusan zai angwance a cikin watan Maris mai kamawa, sai dai ba a san wacece amaryar ba.
Kwatsam babu zato balle tsammani, sai ga furodusan da kansa ya wallafa hotunansa tare da jaruma Aishatul Humaira inda ya bayyana cewa aurenta zai yi.
Kamar yadda wallafar tace: “Zan yi wuff da gishiri ambassador.”
Bayan wallafar da yayi, jaruma Aishatul Humaira ta sake wallafa hotunan a shafinta na Instagram inda ta hada da alamar soyayya.
Sai dai ko bayan bayyanar hotunan, babu takamaiman lokacin auren da Furodusa Abubakar Bashir Maishadda ya sanar ko kuma amarya Aishatul Humaira.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarki Aminu Ado Bayero ya baiwa Alan Waka Sabuwar Sarauta a Masarautar Kano

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Mai martaba Sarkin Kano na 15...

Soke Hawan Sallah: Dole Gwamnatin tarayya ta biya mu diyya – Gwamnatin Kano

Daga Isa Ahmad Getso   Gwamnatin jihar Kano ta bukaci gwamnatin...

NiMet ta bayyana jihohin da za a sami tsawa da ruwan sama na kwanaki 3 a Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta...

Hajjin bana: Gobarar ta tashi a otel din wasu Alhazan Nigeria a Makka

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Hukumar kula da Alhazai ta Najeriya...