Furodusa Abubakar mai shadda na shirin angwancewa da Jaruma Aisha Humaira

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

Kyawawan hotunan kafin aure Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jaruma Aisha Ahmad Idris wacce aka fi sani da Aishatul Humaira sun karade shafukan Sada Zumunta na Facebook da Instagram a safiyar alhamis din nan.

Kadaura24 ta rawaito tun farko dai, an fara rade-radin cewa Furodusan zai angwance a watan Maris, sai dai kuma ba a bayyana wacece amaryar ba.
Da kanshi ya je shafinsa na Instagram inda ya sanar da cewa zai yi wuff da jakadiyar gishirin Dangote tare da saka hotunansu na kafin aure.
A safiyar Alhamis ne aka wayi gari da sabbin kyawawan hotunan kafin aure na furodusa a masana’antar Kannywood, Abba Bashir Maishadda da jaruma Aishatul Humaira.
Tun farko dai, shafin Labaran Kannywood a Twitter a kwanaki biyu da suka gabata sun bayyana cewa furodusan zai angwance a cikin watan Maris mai kamawa, sai dai ba a san wacece amaryar ba.
Kwatsam babu zato balle tsammani, sai ga furodusan da kansa ya wallafa hotunansa tare da jaruma Aishatul Humaira inda ya bayyana cewa aurenta zai yi.
Kamar yadda wallafar tace: “Zan yi wuff da gishiri ambassador.”
Bayan wallafar da yayi, jaruma Aishatul Humaira ta sake wallafa hotunan a shafinta na Instagram inda ta hada da alamar soyayya.
Sai dai ko bayan bayyanar hotunan, babu takamaiman lokacin auren da Furodusa Abubakar Bashir Maishadda ya sanar ko kuma amarya Aishatul Humaira.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...