SADAQATUL JARIYA :Makarantar Islamiyya Na Neman Tallafin a Siya mata Matsuguni

Date:

Daga Abdullahi kano

Makarantar Islammiya ta Madrasatu Zubairu Bin Awwam Litahfizil Qur’an Waddarasatil Islamiyya da ke Unguwar Tunga a karamar hukumar Gwale na neman gudun muwar Bayin Allah domin a siya mata wani kango a unguwar don yin matsuguninta na din din din.

Shugaban Makarantar Malam Abdulrazak Zubairu(Malam Baffa) ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi yayin bikin saukar Dalibai Goma, wanda makarantar islamiyyar ta gudanar a unguwar Tunga , karamar Hukumar Gwale Kano.

 

Yace makarantar ta sami Albarkar dalibai , inda a kullum dalibai sai karuwa suke sai dai rashin wadataccen Muhalli na kawo tarnaki a fannin cigaban da koyar da dalibai ilmin addinin musulunci.

 

“Muna amfani da wani gida , da kuma kofar gidajen alumma a matsayin ajujuwa to lokacin damina da sanyi muna fuskantar kalubale, wasu magada sun bamu aron kangonsu muna koyar da dalibai a ciki, amma yanzu suna bukatar za su siyar, akan kudi Naira miliyan daya da Rabi.”

 

” Muna rokon Bayan Allah wadanda Allah ya horewa , a taimaka a siya mana wannan kangon, domin wata kungiya tayi mana alkawarin indai mun mallaki filin, za su gina mana ajujuwa fi sabi lillah” inji malam Baffa.

Ga duk Mai bukatar taimakawa zai iya tuntubar malam baffa ,  Tunga a kan wadannan lambobi +234 813 660 8606

Yayin bikin saukar karatun Alqur’ani mai girma na dalibai goma, an gudanar da jawabai na Jan hankali da nasihohi don samar da alumma ta Gari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...