Wasu Yara biyu sun Rasa Rayukansu a wani kududdufi a Mariri

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

Wasu Mutane biyu, Umar Auwalu mai shekaru 15 da Muhammed Nafis, 20, a ranar Juma’a sun Rasa Rayukansu a cikin wani kududdufi a Mariri Ramin Kalanzir da ke karamar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Alhaji Saminu Abdullahi, jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a a Kano.

Abdullahi ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa da misalin karfe 07:57 na safe daga wani mai suna Mustapha Musa inda nan take ta aika da jami’an ta zuwa inda lamarin ya faru da misalin karfe 08:10 na safe.

“An fitar da su daga cikin kududdufin kuma daga baya an mika gawarwakinsu ga Dagacin unguwar Sheka Gabas, Alhaji Umar Yunusa,” in ji Abdullahi.

Jami’in Hulda da jama’a na hukumar kashe gobarar ya ce har yanzu ba a gano musabbabin mutuwar su ba, amma ana ci gaba da bincike.

Ya shawarci iyayen yara da kuma masu unguwanni dsu Rika kula da zirga-zirgar ya’yansu a musamman ga wadanda suke kusa da kududdufi don hana faruwar abubuwa irin wadannan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...