Wasu Yara biyu sun Rasa Rayukansu a wani kududdufi a Mariri

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

Wasu Mutane biyu, Umar Auwalu mai shekaru 15 da Muhammed Nafis, 20, a ranar Juma’a sun Rasa Rayukansu a cikin wani kududdufi a Mariri Ramin Kalanzir da ke karamar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Alhaji Saminu Abdullahi, jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a a Kano.

Abdullahi ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa da misalin karfe 07:57 na safe daga wani mai suna Mustapha Musa inda nan take ta aika da jami’an ta zuwa inda lamarin ya faru da misalin karfe 08:10 na safe.

“An fitar da su daga cikin kududdufin kuma daga baya an mika gawarwakinsu ga Dagacin unguwar Sheka Gabas, Alhaji Umar Yunusa,” in ji Abdullahi.

Jami’in Hulda da jama’a na hukumar kashe gobarar ya ce har yanzu ba a gano musabbabin mutuwar su ba, amma ana ci gaba da bincike.

Ya shawarci iyayen yara da kuma masu unguwanni dsu Rika kula da zirga-zirgar ya’yansu a musamman ga wadanda suke kusa da kududdufi don hana faruwar abubuwa irin wadannan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...