ASUU ta ce ta yanke Kauna da Gwamnatin Buhari

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara

 

Kungiyar malama jami’a ta Najeriya ASUU ta nuna shakkunta game da cika alkawuran da gwamnatin shugaba Buhari ta dauka na samar da mafita ga matsalolin da fannin ilimin kasar ke ciki, musammam jami’u.

Kungiyar ta ce za ta fara yajin aikin sai baba ta gani nan ba da jimawa ba.

Kungiyar ta bayyana lamarin da ke faruwa a halin yazu da “abin kunya” yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da kare tsarin biyan kudi na IPPIS duk da zargin cewa akwai almundahana a cikinsa, kamar yadda ya bayyana a cikin rahoton da babban akantan tarayyar Najeriya ya gabatar a gaban Majalisar dattawan kasar.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ASUU ta nuna fushinta kan yadda aka rika zaman sasanci tsakaninta da gwamnati kan yadda za a farfado da ilimi sai dai gwamnati ta gaza dabbaka abin da take ta ikirari a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...