ASUU ta ce ta yanke Kauna da Gwamnatin Buhari

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara

 

Kungiyar malama jami’a ta Najeriya ASUU ta nuna shakkunta game da cika alkawuran da gwamnatin shugaba Buhari ta dauka na samar da mafita ga matsalolin da fannin ilimin kasar ke ciki, musammam jami’u.

Kungiyar ta ce za ta fara yajin aikin sai baba ta gani nan ba da jimawa ba.

Kungiyar ta bayyana lamarin da ke faruwa a halin yazu da “abin kunya” yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da kare tsarin biyan kudi na IPPIS duk da zargin cewa akwai almundahana a cikinsa, kamar yadda ya bayyana a cikin rahoton da babban akantan tarayyar Najeriya ya gabatar a gaban Majalisar dattawan kasar.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ASUU ta nuna fushinta kan yadda aka rika zaman sasanci tsakaninta da gwamnati kan yadda za a farfado da ilimi sai dai gwamnati ta gaza dabbaka abin da take ta ikirari a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare...

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

  Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar...

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...