2023: Sheikh Ibrahim Khalil da Dr Dukawa sun koma jam’iyyar ADC

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

Bayan bayyana ficewarsa daga jam’iyya mai mulki ta APC a karshen shekarar da ta gabata ta 2021, shugaban majalisar malamai ta jihar Kano, Sheik Ibrahim Khalil, ya shiga jam’iyyar ADC, wanda kuma nan gaba kadan za’a shirya taron karbarsa cikin jam’iyyar.

Bayanin komawa jam’iyyar ADC da malamin yayi, na kunshe cikin wani sako da shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Shu’aibu Ungoggo, ya gabatar ga manema labarai a yau juma’a.

Cikin bayanin nasa, Shu’aibu Ungoggo, yace malamin ya shigo jam’iyyar tasu ta ADC ne tare da Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa na jami’ar Bayero, da kuma wasu malaman jami’a guda takwas da suka rufa masa baya, a kokarinsu na ganin cewa an ceto jihar Kano daga halin da ta ke ciki, a cewarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga...

Gwamnatin Jihar Kano ta fara bincike kan mutuwar wasu ɗaliban makarantar Sakandare biyu

  Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Makoda, ya...

Kamfanin Yahuza Suya Ya aike da Sakon ta’aziyyar Rasuwar tsohon shugaban Kasa Buhari

Shugaban kamfanin Yahuza Suya and Catering Services Nig. Limited,...

Yadda aka Binne Gawar Buhari a gidansa dake Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...