2023: Sheikh Ibrahim Khalil da Dr Dukawa sun koma jam’iyyar ADC

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

Bayan bayyana ficewarsa daga jam’iyya mai mulki ta APC a karshen shekarar da ta gabata ta 2021, shugaban majalisar malamai ta jihar Kano, Sheik Ibrahim Khalil, ya shiga jam’iyyar ADC, wanda kuma nan gaba kadan za’a shirya taron karbarsa cikin jam’iyyar.

Bayanin komawa jam’iyyar ADC da malamin yayi, na kunshe cikin wani sako da shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Shu’aibu Ungoggo, ya gabatar ga manema labarai a yau juma’a.

Cikin bayanin nasa, Shu’aibu Ungoggo, yace malamin ya shigo jam’iyyar tasu ta ADC ne tare da Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa na jami’ar Bayero, da kuma wasu malaman jami’a guda takwas da suka rufa masa baya, a kokarinsu na ganin cewa an ceto jihar Kano daga halin da ta ke ciki, a cewarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...