Daga Albdulmajid Isa Tukuntawa
Mai Taimakawa gwamnan jihar Kano a kan harkokin da suka shafi kasuwar kanti kwari Alh usman nagoda, ya rabawa mata da maza tallafin kudi naira dubu biyar biyar domin su dogara da kawunansu.
Da yake jawabi a wajen usman nagoda ya bayar da tallafin ne domin inganta rayuwar al’umma da kuma rage talauci a cikin al’umma kamar yadda Gwamna Ganduje yake yi a kowanne lokaci.
“Ba iya haka wannan tallafi zai tsayaba akwai kashi na biyu wanda zai zo bada jimawa ba, muna fatan zaku yi amfani da abun da kuka samu wajen inganta sana’o’inku don mu cimma kudirin da ya sanya aka baku wannan tallafi”. Inji Nagoda
Maitaimakawa gwamnan ya taya wadanda suka amfana da tallafin murnar samun tallafin, sannan yayi fatan cigaba da tallafawa al’umma don inganta rayuwarsu.
wasu da suka amfana sun baiyana jindadinsu tare da Alkawari alkinta dukiyar da aka basu ta hanyar da ta dace.
Kadaura24 ta rawaito matasa maza da mata ki manin Dari uku ne suka amfana da Tallafin kudin na naira dubu biyar-biyar kowannensu .wasu da suka amfana sunbaiyana jindadinsu tare da Alkawari Alkinta dukiyar tasu ta hanyar da yadac