Hadimin Ganduje SSA Gwarmai ya sake rabawa matasa kudi, Mashina da Jakai don inganta Rayuwarsu

Date:

Daga Sayyeed Abubakar

 

Mataimaki na musamman ga Gwamna jihar kano a kan harkokin matasa Alhaji Murtala Gwarmai ya rabawa matasa guda shida babura domin saukaka musu a sha’anin sufuri a wani yunkuri na basu damar sharbar romon damakaradiyya.

Da yake zantawa da manema labarai Alhaji Murtala Gwarmai yace ya rabawa matasa babura da jakunan ne domin cika umarnin gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje na tallafawa mata da matasa don inganta rayuwarsu kamar yadda yake yi a matakin jihar.

Gwarmai yace ya zama wajibi ya bada tallafin saboda irin gudunmawar da suka baiwa gwamnatin kano musamman a zaben shekara ta 2019 da ya gabata, da kuma kokarin da suke yi na ganin sun dogara da kawunansu.

A yau mun bada babura guda shida ga matasa sannan daya daga cikinsu yace shi jakai yake bukata domin inganta harkokinsa na Neman abinchi wanda yake gudanarwa don ya rufawa Kansa asiri”. Inji Gwarmai.

Bayan ya rabon baburan Hadimin na Ganduje ya baiwa wasu matasa 4 tallafin naira dubu Dari biyu da hamsin kowannensu tare kuma da mikawa wata mata takardar shidar daukar aiki a ma’aikatar lafiya ta jihar kano.

ina so Ku sani na baku waɗanan babura da kudin ne saboda ku ma Ku sharbi romon damakaradiyya, kuma Mai gidanmu Hon. Murtala Sule Garo ya taka rawa sosai wajen tabbatuwar wannan al’amari don haka idan kuka gidewa Gwamna Ganduje to Ku godewa Hon. Murtala Sule Garo sannan kuma Nima sai ku rabani cikin godiyar”.
Inji SSA Gwarmai

Mai kudi meku da Muhd sani sabalanga na daga cikin wadanda suka amfana da tallafin na wannan lokaci sun godewa Hon Murtala Sule Garo da Hon. Murtala Gwarmai bisa abun alkhairin da S SA din yayi musu, tare kuma da bada tabbacin yin amfani da tallafin ta hanyar data dace.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...