Rundunar Yan Vigilantee ta Kama Wani Matashi da ake zargi da satar Awaki a Sumaila

Date:

Daga Rabi’u Usman

Rundunar Vigilantee ta Jihar Kano ta ce ta Samu Nasarar Dakume Wani Matashi Mai Suna Yunusa da ake Zargin Barawon Awakin Jama’a ne.

Rundunar tace Wannan ba Shi ne farau ba da aka taba Kama Wannan Matashi da Zargin Satar Dabbobin Jama’a ba, Wanda yanzu Haka Dubun Sa ta Cika Bayan da aka Kama Shi da Zargin Satar Awakai guda 3 da Kimar Kudin Su takai Dubu 100.

Babban Kwamandan Rundunar Muhammad Kabir Alhaji ne ya Bayyana hakan yayin da yake Ganawa da Manema Labarai a Wannan rana.

A Nasa Bangaren Matashi Yunusa da ake Zargin Barawon Awakin Jama’a ne ya Bayyana Cewar, ya Sato su a Cikin Daji ne Sannan ya Kawo Su Kasuwar Gomo dake Cikin Karamar Hukumar Sumaila a Nan Kano Amma tsautsayi ne.

A Karshe dai Kwamandan yayi Kira ga Al’umma dasu Kasance Masu Taimakawa Jami’an Rundunar Vigilantee da Bayanan Sirri da Zarar Sunga Motsin Abin da Basu Amince da Shi ba Domin Kawo Musu Dauki na Gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...