Rundunar Yan Vigilantee ta Kama Wani Matashi da ake zargi da satar Awaki a Sumaila

Date:

Daga Rabi’u Usman

Rundunar Vigilantee ta Jihar Kano ta ce ta Samu Nasarar Dakume Wani Matashi Mai Suna Yunusa da ake Zargin Barawon Awakin Jama’a ne.

Rundunar tace Wannan ba Shi ne farau ba da aka taba Kama Wannan Matashi da Zargin Satar Dabbobin Jama’a ba, Wanda yanzu Haka Dubun Sa ta Cika Bayan da aka Kama Shi da Zargin Satar Awakai guda 3 da Kimar Kudin Su takai Dubu 100.

Babban Kwamandan Rundunar Muhammad Kabir Alhaji ne ya Bayyana hakan yayin da yake Ganawa da Manema Labarai a Wannan rana.

A Nasa Bangaren Matashi Yunusa da ake Zargin Barawon Awakin Jama’a ne ya Bayyana Cewar, ya Sato su a Cikin Daji ne Sannan ya Kawo Su Kasuwar Gomo dake Cikin Karamar Hukumar Sumaila a Nan Kano Amma tsautsayi ne.

A Karshe dai Kwamandan yayi Kira ga Al’umma dasu Kasance Masu Taimakawa Jami’an Rundunar Vigilantee da Bayanan Sirri da Zarar Sunga Motsin Abin da Basu Amince da Shi ba Domin Kawo Musu Dauki na Gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...