Rundunar Yan Vigilantee ta Kama Wani Matashi da ake zargi da satar Awaki a Sumaila

Date:

Daga Rabi’u Usman

Rundunar Vigilantee ta Jihar Kano ta ce ta Samu Nasarar Dakume Wani Matashi Mai Suna Yunusa da ake Zargin Barawon Awakin Jama’a ne.

Rundunar tace Wannan ba Shi ne farau ba da aka taba Kama Wannan Matashi da Zargin Satar Dabbobin Jama’a ba, Wanda yanzu Haka Dubun Sa ta Cika Bayan da aka Kama Shi da Zargin Satar Awakai guda 3 da Kimar Kudin Su takai Dubu 100.

Babban Kwamandan Rundunar Muhammad Kabir Alhaji ne ya Bayyana hakan yayin da yake Ganawa da Manema Labarai a Wannan rana.

A Nasa Bangaren Matashi Yunusa da ake Zargin Barawon Awakin Jama’a ne ya Bayyana Cewar, ya Sato su a Cikin Daji ne Sannan ya Kawo Su Kasuwar Gomo dake Cikin Karamar Hukumar Sumaila a Nan Kano Amma tsautsayi ne.

A Karshe dai Kwamandan yayi Kira ga Al’umma dasu Kasance Masu Taimakawa Jami’an Rundunar Vigilantee da Bayanan Sirri da Zarar Sunga Motsin Abin da Basu Amince da Shi ba Domin Kawo Musu Dauki na Gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...