Yanzu-Yanzu: An Sako Dalibai 27 na Makarantar Gandun Daji ta kaduna

Date:

Daliban nan 27 da aka sace daga Kwalejin Koyon Gandun Daji ta Tarayya, Afaka, jihar Kaduna, an sake su.


 Daya daga cikin mutanen da suka karbi daliban ya tabbatar wa Daily Trust labarin.

 Ya ce kwamitin tattaunawa na Sheikh Ahmed Gumi ne ya taimaka wajen sakin tare da goyon baya daga tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo.


 Daliban na daga cikin mutane 37 da aka sace kusan watanni biyu da suka gabata.
 Bayan biyan kudin fansa daga iyaye da shugabannin makarantar, ‘yan fashin sun saki 10 kawai daga cikin wadanda aka yi garkuwar da su.


 Da farko wadanda suka sace su sun nemi gwamnatin jihar Kaduna ta ba su kudin fansa har Naira miliyan 500 amma Gwamna Nasir El-Rufai ya yi watsi da batun tattaunawar, yana mai cewa ‘yan bindiga sun cancanci kashewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...