Yanzu-Yanzu: An Sako Dalibai 27 na Makarantar Gandun Daji ta kaduna

Date:

Daliban nan 27 da aka sace daga Kwalejin Koyon Gandun Daji ta Tarayya, Afaka, jihar Kaduna, an sake su.


 Daya daga cikin mutanen da suka karbi daliban ya tabbatar wa Daily Trust labarin.

 Ya ce kwamitin tattaunawa na Sheikh Ahmed Gumi ne ya taimaka wajen sakin tare da goyon baya daga tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo.


 Daliban na daga cikin mutane 37 da aka sace kusan watanni biyu da suka gabata.
 Bayan biyan kudin fansa daga iyaye da shugabannin makarantar, ‘yan fashin sun saki 10 kawai daga cikin wadanda aka yi garkuwar da su.


 Da farko wadanda suka sace su sun nemi gwamnatin jihar Kaduna ta ba su kudin fansa har Naira miliyan 500 amma Gwamna Nasir El-Rufai ya yi watsi da batun tattaunawar, yana mai cewa ‘yan bindiga sun cancanci kashewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...