Yanzu-Yanzu: An Sako Dalibai 27 na Makarantar Gandun Daji ta kaduna

Date:

Daliban nan 27 da aka sace daga Kwalejin Koyon Gandun Daji ta Tarayya, Afaka, jihar Kaduna, an sake su.


 Daya daga cikin mutanen da suka karbi daliban ya tabbatar wa Daily Trust labarin.

 Ya ce kwamitin tattaunawa na Sheikh Ahmed Gumi ne ya taimaka wajen sakin tare da goyon baya daga tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo.


 Daliban na daga cikin mutane 37 da aka sace kusan watanni biyu da suka gabata.
 Bayan biyan kudin fansa daga iyaye da shugabannin makarantar, ‘yan fashin sun saki 10 kawai daga cikin wadanda aka yi garkuwar da su.


 Da farko wadanda suka sace su sun nemi gwamnatin jihar Kaduna ta ba su kudin fansa har Naira miliyan 500 amma Gwamna Nasir El-Rufai ya yi watsi da batun tattaunawar, yana mai cewa ‘yan bindiga sun cancanci kashewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...