Zaftare albashi zai sa ma’aikata cikin kunci – Kungiyar Kwadago

Date:

Kungiyar kwadago ta Najeriya ta gargadi gwamnatin tarayya da ta dakatar da yunkurin da take yi na rage albashin ma’aikata, tana mai cewa irin wannan mataki zai sa ma’aikata su shiga cikin wani hali na ha’u’la’i.

A ranar Talata ne minister kudi ta Najeriya Zainab Ahmed Shamsuna ta bayyana cewa gwamnati na nazari akan yadda za ta zaftare yawan kuɗaɗen da take kashewa ta hanyar rage albashin ma’aikata.

Rahotanni sun kuma ce ministar ta umarci hukumar albashin ma’aikata ta yi nazari akan albashi da yawan ma’aikatun gwamnati da ke kasar.

Manyan kungiyoyin kwadago hudu da ke yajin aiki a Najeriya
May Day: Kalubalen da ma’aikatan gwamnati suke fuskanta a Najeriya
Sai dai shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya, Ayuba Wabba ya yi kira ga gwamnati a kan ka da ta zaftare albashin mafi kankanta na naira dubu talatin na ma’aikata, yana mai cewa albashin masu karbar albashi mai tsoka ne kawai ya kamata a rage musamman masu rike da mukaman siyasa.

“Abu ne da ba za a taɓa tsammani ba cewa gwamnati za ta yi niyya ta rage albashin ma’aikatan Najeriya a wannan lokacin”.

”Tambayar anan ita ce shin wani albashi ne gwamnati za ta zaftare? Ko shakka babu ba albashi mafi kankanta na naira dubu talatin ba ne wanda halin yanzu ba ya iya sayan buhun shinkafa.

Shugaban kungiyar kwadagon, yayin da yake bayyana matakin a matsayin “rashin tausayi” da “rashin tunani”, ya ce ma’aikatan Najeriyar na bukatar a gaggauta janyewar matakin tare da neman afuwa daga Ministan Kudin kasar.

157 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...