An Kaddamar da littafi Mai taken “So ake yiwa Annabi ko Kauna” 

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam
Wata Kungiyar mai suna alkalami ya zarta takobi da hadin gwiwar  gaskiya dokin karfe karkashin jagorancin Malam Naziru Musa Shehu Marmara ta kaddamar da wani Littafi Mai takenbSo ake yiwa Annabi S A W wanda ya kunshi bayani Kan soyayyar Ma’aikin Allah (S A W).
Malam Naziru Musa Marmara shi ya rubuta Littafin Kuma a zantarsa da wakilin Kadaura24 yace ya rubuta Littafin ne da nufin kara cusawa al’umma son Manzon Allah A W tare Kuma da banbance irin son da za a yiwa Ma’aikin .
“Littafin ya yi bayani sosai Kan irin nau’in soyayya da Kuma Kauna ,tare da bayyana irin Wacce za a yiwa Ma’aikin Allah tsira da aminchin Allah su tabbata a gare shi, don Haka muke ganin Littafin Zai amfanar da al’ummar Musulmi sosai’ Inji Mal Naziru Marmara 
 
Malam Naziru Marmara ya Kara da Cewa an kaddamar da littafin ne domin tinasar da al’umma so za a yiwa Annabi ko kauna za’a nunawa Masa da Kuma yadda za a yi.
Yayin taron an Karrama Wasu Mutane Waɗanda Shugaban kungiyar malam naziru ya ce sun karrama mutanan ne saboda jajircewar su wajan hidimtawa al’umma .
Waɗanda aka karrama sun hada da Sheikh Askiya Sheikh Nasiru Kabara Sai Mai Wuddadu da Usman Muhammad Tahir mai dubun Isa da dai sauran su.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...