Yanzu-Yanzu: Gwamnan Ekiti da na Jigawa sun ambaci Ɗanzago da Shugaban APC a Kano

Date:

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Ekiti da na Jigawa sun ambaci Ɗanzago da shugaban APC a Kan

Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, da takwaransa na Jigawa, Abubakar Badaru, sun kira Ahmadu Haruna Zago da shugaban jam’iyar APC a Jihar Kano.

Wannnan al’amari daya faru wata alama ce da za a iya cewa ta faru ta ƙare a shugabancin APC bayan da Fayemi, wanda shine Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya, da Badaru, su ka kira Ɗanzago da shugaban jam’iyar APC a Kano.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa gwamnonin, a yau Asabar, yayin jawabin su a wajen taron cikar shekarar Cibiyar Bincike kan Dimokraɗiyya ta Aminu Kano da ke ƙarƙashin Jami’ar Bayero shekaru 21, kowannen su ya kira Ɗanzago da shugaban jam’iyar APC a yayin shimfiɗa a jawaban su.

Jaridar ta ƙara da cewa, wannan shi ne karo na farko da a ka ambata Ɗanzago a matsayin shugaban APC a bainar jama’a, tun bayan da a ka yi zaɓen Shugabannin jam’iyar a Kano.

Tun a lokacin zaɓen shugabannin jam’iya na jiha a ka samu rabuwar APC gida biyu, inda ɓangaren Ganduje ya zaɓi Abdullahi Abbas a matsayin shugaba, shi kuma tsagin Shekarau ya zaɓi Ɗanzago.

Sai dai kuma, a ranar Talatar da ta gabata ne wata babbar kotu a Abuja ta rushe shugabacin Abdullahi Abbas ta kuma tabbatar da na Ɗanzago a jihar, duk da cewa tsagin Gandujen sun ce za su ɗaukaka ƙara.

23 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...