Yanzu-Yanzu: Gwamnan Ekiti da na Jigawa sun ambaci Ɗanzago da Shugaban APC a Kano

Date:

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Ekiti da na Jigawa sun ambaci Ɗanzago da shugaban APC a Kan

Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, da takwaransa na Jigawa, Abubakar Badaru, sun kira Ahmadu Haruna Zago da shugaban jam’iyar APC a Jihar Kano.

Wannnan al’amari daya faru wata alama ce da za a iya cewa ta faru ta ƙare a shugabancin APC bayan da Fayemi, wanda shine Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya, da Badaru, su ka kira Ɗanzago da shugaban jam’iyar APC a Kano.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa gwamnonin, a yau Asabar, yayin jawabin su a wajen taron cikar shekarar Cibiyar Bincike kan Dimokraɗiyya ta Aminu Kano da ke ƙarƙashin Jami’ar Bayero shekaru 21, kowannen su ya kira Ɗanzago da shugaban jam’iyar APC a yayin shimfiɗa a jawaban su.

Jaridar ta ƙara da cewa, wannan shi ne karo na farko da a ka ambata Ɗanzago a matsayin shugaban APC a bainar jama’a, tun bayan da a ka yi zaɓen Shugabannin jam’iyar a Kano.

Tun a lokacin zaɓen shugabannin jam’iya na jiha a ka samu rabuwar APC gida biyu, inda ɓangaren Ganduje ya zaɓi Abdullahi Abbas a matsayin shugaba, shi kuma tsagin Shekarau ya zaɓi Ɗanzago.

Sai dai kuma, a ranar Talatar da ta gabata ne wata babbar kotu a Abuja ta rushe shugabacin Abdullahi Abbas ta kuma tabbatar da na Ɗanzago a jihar, duk da cewa tsagin Gandujen sun ce za su ɗaukaka ƙara.

23 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...