Hisbah ta kama mutane 25 bisa zargin shirya auren jinsi a Kano

Date:

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama akalla mutane 25 bisa zargin shirya auren jinsi a unguwar Hotoro da ke cikin birnin Kano.

Mataimakin Kwamandan Hukumar, Mujahedeen Aminudeen, ne ya tabbatar da kamun a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a ranar Lahadi.

A cewarsa, jami’an hukumar sun cafke wadanda ake zargin — maza 18 da mata bakwai — a cibiyar taro ta Fatima Event Centre da ke kan hanyar Hotoro Bypass a ranar Asabar.

“Yau Asabar, 25 ga Oktoba, 2025, mun samu rahoton cewa wasu mutane na shirin yin auren ‘Jinsi. Nan take jami’anmu suka dira cibiyar taron Fatima Event Centre, inda aka shirya wannan haramtaccen taron, kuma suka kama mutane 25,” in ji Aminudeen.

Ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin, ciki har da wanda ake kira ango, daga yankuna daban-daban kamar Sheka, Yar Gaya, da Kofar Nasarawa.

Mataimakin Kwamandan ya gargadi cewa hukumar ba za ta zauna ba ta bar wasu marasa tarbiyya su bata sunan Kano ba.

“Muna kira ga jama’ar jihar da su ci gaba da baiwa hukumar hadin kai ta hanyar kawo rahoton duk wani abu da ya shafi rashin tarbiyya a cikin al’umma. Hukumar Hisbah za ta ci gaba da kai samame a wuraren da ke yada alfasha,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...