Al’ummar Tsanyawa Sun ce Murtala Garo ya Fitar dasu daga Halin kaka Nikayin Ruwan Sha

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
Shugaban Karamar Hukumar Tsanyawa Alhaji Kabiru Sulaiman Dumbulun ya yabawa Kwamishinan Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar Kano Alhaji Murtala Sule Garo bisa sahallewa da yayi aka gina Rijiyoyin Burtsatse Masu Amfani da hasken Rana Guda biyi da Kuma na tuku-tuka Guda biyu a yankinsa.
Shugaban Karamar Hukumar Tsanyawa Wanda mataimakinsa Alhaji Tijjani Abubakar ‘yan kamaye ya Wakilta ya bayyana hakan ne yayin bikin bude Rijiyoyin Burtsatse a Garin Dumbulun.
Shugaban Karamar Hukumar yace yabon ya Zama wajibi Idan akai la’akari da yadda Aikin Zai taimakawa Rayuwar al’ummar da aka Gudanar musu da aiki, Saboda yadda aikin zai fitar da al’ummar yankin daga halin rashin ruwan Sha.
Yace Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Dr Abdullahi Umar Ganduje ta dauki batun Samar da tsaftataccen Ruwan Sha ga al’umma da muhimmancin, Inda yace hakan ce tasa Karamar Hukumar ta Gudanar da Aikin domin inganta Rayuwar Al’ummar yankin.
Shugaban ya Kara da Cewa an Samar da Rijiyoyin Burtsatse Mai Amfani da hasken Ranar a sakatariyar Karamar Hukumar da Kuma Garin Dumbulum. Yayin da aka Samar da na tuku-tuka a Garin Kabagiwa Gidan Alaramma da Gidan Tuku unguwar Makama dukkanin wuraren yace a baya sun dade Suna fama da Matsalar ta Rashin Ruwa.
A Jawabinsu daban-daban Dagacin Garin Dumbulum Alhaji Nasiru Adamu dana Kabagiwa Malam Umar Zubairu Kabagiwa sun yabawa Majalisar Karamar Hukumar ta Tsanyawa da Kwamishina Murtala Sule Garo bisa Gudunmawar da Suka bayar wajen tabbatuwar Aikin Rijiyoyin Burtsatsen.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...