Abun Alkhairin da mataimakin gwamnan Kano ya yi min ba a taba yin min shi a duniya ba – Kabiru D Bello

Date:

Tsohon Dan takarar shugaban karamar hukumar Gwarzo Alhaji Kabiru D Bello ya yabawa mataimakin Gwamnan jihar Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo bisa yadda ya taimakawa mutane da yawa domin sauke farali a bana .

” Tabbas abun alkhairin da mataimakin gwamnan ya yi min ba abun da zan ce sai godiya, ya taimake ni na sauke farali a Wannan Shekarar, don haka ya yi min abun da ba wanda ya taba yi min a rayuwata”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Alhaji. Kabiru D Bello ya bayyana hakan ne a wata zantawa da ya yi da wakilin Kadaura24 a birnin Makka.

Gidajen Wasanni a Kano sun bi ka’dojin da muka sanya musu yayin bikin sallah – Abba El-Mustapah

” Ranar da mataimakin gwamnan ya sanar da ni cewa ya saka ni cikin wadanda za su je kasar Saudiyya domin yin aikina na Kula da lafiya kuma in sauke farali, a ranar kwata-kwata na Kasa samun nutsuwa kuma ban yi bacci ba saboda farin ciki”. Inji Kabiru Bello

Alhaji Kabiru D Bello ya ce mataimakin gwamnan yana tallafawa matasa sosai domin inganta rayuwarsu don su dogara da kawunansu.

InShot 20250309 102403344

” Ina kuma godewa mai gayya mai aiki balaraben gwamnan Kanawa, Alhaji Abba Kabir Yusuf , saboda yadda yake gudanar da aiyukan cigaba domin bunkasa jihar Kano”.

Ya yi Addu’ar Allah ya sakawa mataimakin Gwamnan da mafificin alkhairi ya sake daga darajarsa domin ya cigaba da taimakawa rayuwar al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...