Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf ta ware kudi domin sake gina masallacin da wani mutum ya bankawa wasu masallata wuta yayin da suke sallar asuba a karamar hukumar Gezawa.

A wata sanarwa da jami’in yada labaran yankin Jamilu Mustapha Yakasai ya aikowa Kadaura24, ya ce Shugaban karamar hukumar Gezawa, Alhaji Mukaddas Bala Jogana, ya bayyana cewa, baya ga sake gina masallacin, gwamnatin za ta kuma gina ajujuwa, da bandakuna, da rijiyar burtsatde a harabar masallacin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Mukaddas ya kara da cewa gwamnatin jihar ta kammala aikin titin kilomita 5 na karamar hukumar.

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Ya yi kira ga ma’aikatar ayyuka da ta fara aikin titin Dan Madanho zuwa Kwasangwami zuwa Zango, wadda ya ce hanya ce mai muhimmanci da al’umma da dama ke amfani da ita.

Alhaji Mukaddas Bala ya nuna matukar godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kokarinsa na daukaka martabar jihar Kano. Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su ci gaba da marawa gwamnatin gwamna Abba Kabir Yusuf baya.

InShot 20250309 102403344

Shugaban karamar hukumar Gezawan ya yi alkawarin za’a ci gaba da gudanar da ayyukan raya kasa don amfanin al’ummar yankin, musamman a fannonin kiwon lafiya, ilimi, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...