Obasanjo, Atiku, Obi da sauransu sun halarci taron kaddamar da littafin Sule Lamido

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo, da Tsoffin Mataimakan Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, Namadi Sambo da Tsoffin Shugabannin Majalisar Dattawa, Ken Nnamani, Paius Ayim sun isa wurin taron kaddamar da littafin tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido.

Kadaura24 ta rawaito tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, shi ake sa ran zai duba littafin tarihin rayuwar Lamido mai suna “Being True to Myself”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

 

Daga cikin wadanda suka halarci taron kaddamar da littafin da ake gudanarwa a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja, akwai dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, sannan gwamnonin Gombe, Muhammadu Yahaya; Jigawa, Umar Namadi; da Plateau, Caleb Mutfwang.

InShot 20250309 102403344

Haka kuma akwai manyan mutane da suka halarci taron, wadanda suka hada da tsohon Gwamna Gabriel Suswam (Benue), Ahmed Makarfi (Kaduna), da Babangida Aliyu (Niger), (Cross Rivers), Liyel Imoke da dai sauransu.

Cikakken bayani na nan tafe

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...