Obasanjo, Atiku, Obi da sauransu sun halarci taron kaddamar da littafin Sule Lamido

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo, da Tsoffin Mataimakan Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, Namadi Sambo da Tsoffin Shugabannin Majalisar Dattawa, Ken Nnamani, Paius Ayim sun isa wurin taron kaddamar da littafin tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido.

Kadaura24 ta rawaito tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, shi ake sa ran zai duba littafin tarihin rayuwar Lamido mai suna “Being True to Myself”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

 

Daga cikin wadanda suka halarci taron kaddamar da littafin da ake gudanarwa a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja, akwai dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, sannan gwamnonin Gombe, Muhammadu Yahaya; Jigawa, Umar Namadi; da Plateau, Caleb Mutfwang.

InShot 20250309 102403344

Haka kuma akwai manyan mutane da suka halarci taron, wadanda suka hada da tsohon Gwamna Gabriel Suswam (Benue), Ahmed Makarfi (Kaduna), da Babangida Aliyu (Niger), (Cross Rivers), Liyel Imoke da dai sauransu.

Cikakken bayani na nan tafe

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...