Gwamna Kano zai Baiwa Malaman Makarantu Bashin Ababen Hawa Motoci Naira Miliyan 200 A Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya amince da kashe Naira miliyan 200 domin sayo ababen hawa don bayar da su bashi ga malaman makarantun firamare da sakandare a fadin jihar,

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24, ya ce za a samar da ababen hawan ga malaman ne a wani mataki na inganta jin dadin ma’aikata da kuma zaburar da ma’aikatan koyarwa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

An tsara tsarin ba da bashin ne don taimaka wa malamai don su mallakin ababen hawa cikin sauki da kuma sauƙaƙa musu ƙalubalen sufuri da suke fuskanta.

Gwamna Yusuf ya bayyana hakan ne a lokacin bikin kaddamar da rabon kayan koyarwa ga makarantun gwamnati, a wani bangare na sake fasalin ilimi na gwamnatin sa.

Za mu yi aikin hanyar Utai zuwa Kademi – Shugaban karamar hukumar Wudil

“Mun fahimci rawar da malamai ke takawa wajen inganta makomar ‘ya’yanmu, wannan shirin bayar da lamuni na daya daga cikin manyan dabarunmu na tallafa wa jin dadin su da kuma bunkasa aikin koyarwa a jihar Kano,” inji gwamnan.

InShot 20250309 102403344

Gwamna Yusuf ya jaddada kudirinsa na inganta samar da ababen more rayuwa musamman a bangaren da ya shafi ilimi, inda ya bayyana malamai a matsayin ginshikin ci gaban kowacce al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...