Za mu yi aikin hanyar Utai zuwa Kademi – Shugaban karamar hukumar Wudil

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban karamar hukumar Wudil Abba Muhammad Tukur ya sha alwashin yin aikin hanyar da ta tashi daga garin Utai na karamar hukumar Wudil zuwa garin Kademi na karamar hukumar Gaya.

Kadaura24 ta rawaito wani Kabiru Isa Tata Kademi ne ya roki shugaban karamar hukumar da ya yi wa Allah da Manzonsa ya yi musu aikin hanyar data tashi daga Utai zuwa kashe a sashin mayar da martani (Comment section) na shafin Facebook na Arewa Radio.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Nan take kuma shugaban karamar hukumar ta Wudil Abba Muhammad Tukur ya mayar masa da martani cikin lafuza masu dadi.

“Insha Allah za mu duba yiwuwar yinta (hanyar Utai zuwa Kademi) Ka san aikin ya hada kananan hukumomin guda biyu (Wudil da Gaya)”. Inji shugaban karamar hukumar Wudil

Ku cusawa mutane kishin jihar Kano don ba mu da jihar da ta fita – Waiya ga Limamai

Wannan ta sa kadaura24 ta tuntubi Babban mai taimakawa shugaban karamar hukumar kan harkokin yada labarai Abba Ashiru, inda ya ba mu tabbacin tunda shugaban ya yi wancan alwashin to babu shakka zai aikin nan ba da jimawa ba.

” Ai tunda Abba Muhammad Tukur har ya yi masa martani ko ya ba shi amsa nan take nasan nan ba da jimawa ba, za a fara aikin saboda muhimmancin da hanyar ke da ita”. Inji Abba Ashiru

InShot 20250309 102403344

Tabbas mutane da yawa suna amfana da aikin kuma idan aka yi aikin zai saukakawa al’ummar kananan hukumomin wudil da Gaya. Kai wai dai nasan aikin zai zama na hadin gwiwa ne tsakanin Wudil da Gaya kuma da zarar komai ya daidaita za’a fara aikin hanyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...