Za mu yi aikin hanyar Utai zuwa Kademi – Shugaban karamar hukumar Wudil

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban karamar hukumar Wudil Abba Muhammad Tukur ya sha alwashin yin aikin hanyar da ta tashi daga garin Utai na karamar hukumar Wudil zuwa garin Kademi na karamar hukumar Gaya.

Kadaura24 ta rawaito wani Kabiru Isa Tata Kademi ne ya roki shugaban karamar hukumar da ya yi wa Allah da Manzonsa ya yi musu aikin hanyar data tashi daga Utai zuwa kashe a sashin mayar da martani (Comment section) na shafin Facebook na Arewa Radio.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Nan take kuma shugaban karamar hukumar ta Wudil Abba Muhammad Tukur ya mayar masa da martani cikin lafuza masu dadi.

“Insha Allah za mu duba yiwuwar yinta (hanyar Utai zuwa Kademi) Ka san aikin ya hada kananan hukumomin guda biyu (Wudil da Gaya)”. Inji shugaban karamar hukumar Wudil

Ku cusawa mutane kishin jihar Kano don ba mu da jihar da ta fita – Waiya ga Limamai

Wannan ta sa kadaura24 ta tuntubi Babban mai taimakawa shugaban karamar hukumar kan harkokin yada labarai Abba Ashiru, inda ya ba mu tabbacin tunda shugaban ya yi wancan alwashin to babu shakka zai aikin nan ba da jimawa ba.

” Ai tunda Abba Muhammad Tukur har ya yi masa martani ko ya ba shi amsa nan take nasan nan ba da jimawa ba, za a fara aikin saboda muhimmancin da hanyar ke da ita”. Inji Abba Ashiru

InShot 20250309 102403344

Tabbas mutane da yawa suna amfana da aikin kuma idan aka yi aikin zai saukakawa al’ummar kananan hukumomin wudil da Gaya. Kai wai dai nasan aikin zai zama na hadin gwiwa ne tsakanin Wudil da Gaya kuma da zarar komai ya daidaita za’a fara aikin hanyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...