Ba mafita ga yi wa Bello Turji Afuwa – kungiyar Hausawan Nigeria

Date:

Daga Saminu Ibrahim Magashi

 

Kungiyar Hausawan Nigeria ta ce ba ta goyon bayan gwamnatin tarayya ta yafe ko ta sasanta da yan taa’addan da suke kashe al’ummar arewacin Nigeria .

” Mun sami labarin wasu Shugabannin fulani da sauran masu ruwa da tsaki suna ta bibiyar gwamnatin tarayya da ta yafewa gawurtaccen dan taa’addan da ya yi kaurin suna wajen kashe al’umma wato Bello Turji, inda ya ce kungiyarsu ga ta goyon bayan wannan matakin”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Shugaban kungiyar Abdullahi Abdullahi ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a jihar Kano ranar litinin.

Ya ce ya zama wajibi Hausawan Nigeria su fito domin nuna damuwarsu kan mawuyacin halin da Hausawa suke ciki, inda ya ce za su yi duk mai yiwuwa wajen domin yakar matsalar tsaro da cin kashin da ake yiwa Hausawa a Nigeria.

Kungiyar FULDAN ta bukaci gwamnatin tarayya ta kawo karshen rikice-rikice a yankun da Fulani ke rayuwa

” Muna so mu ji inda aka kwana a kisan Killar da aka yiwa Sarkin Gobir da mutanen da aka kone a hanyarsu ta Sokoto da kuma na kwana-kwanan nan Mafarautan da aka kashe a Jihar Edo, har yanzu ba mu komai ba, kuma muna bukatar a dauki matakan da suka dace”. Inji Abdullahi Abdullahi

Shugaban kungiyar Hausawa ta Nigeria ya ce akwai bukatar dukkanin masu ruwa da tsaki a cikin al’umma musamman na yankin Jihohin Katsina Sokoto Zamfara da Kebbi da su tashi tsaye wajen kare kawunansu.

InShot 20250309 102403344

Ya kuma kalubalanci gwamnatin jihar Katsina bisa yadda ta kasa fitowa ta sanar da Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu matsalolin tsaro da suka addabi al’ummar jihar, ya ce mai makon a fito da matsalolin sai aka cewa shugaban kasar babu wata matsala.

Daga karshe ya kuma jaddada cewa sun samar da kungiyarsu ne ba don cin mutuncin wasu mutane ko cewa wata kabila yan taa’adda ne ba, sai don hada kan Hausawa da kuma yin magana da murya daya musamman wajen fito da matsalolin da suke damun Hausawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...