Ba a ga watan Zulqida a Nigeria ba – Sarkin Musulmi

Date:

Daga Unmahani Abdullahi Adakawa

 

Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya tabbatar da cewa ba a ga watan Zulqida a jiya lahadi a Nigeria ba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci na fadar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka aikowa manema labarai.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sanarwar ta ce sakamakon rashin ganin watan a jiya lahadi, watan Shawwal zai cika kwanaki 30 cif-cif.

“Gobe talata 29 ga watan Afirilu it ce za ta zamo 1 ga watan Zulqida na wannan shekara ta 1446.

Da dumi-dumi: Sarki Aminu ya nada sabon Galadiman Kano

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar asabar ne fadar Sarkin Musulmi ba da umarnin fara duban watan na zulqada.

InShot 20250309 102403344

Haka ita ma kasar Saudiyya ta ba da sanarwar cewa ba a ga watan na Zulqida a fadin kasar ba don haka watan Shawwal zai cika kwanaki 30.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...